Burkina Faso da Mali da Nijar sun tattauna domin ƙarfafa rundunar haɗin gwiwar ƙasashensu

Ministocin tsaron ƙasashen Burkina Faso da Mali da Jamhuriyar Nijar sun gudanar da taro a Ouagadougou ranar 10 ga Yuli domin duba matakan da za su ɗauka domin ƙarfafa rundunar haɗin gwiwar ƙasashen ƙungiyar Alliance of Sahel States (AES), kamar yadda RFI ta ruwaito a ranar 11 ga Yuli.
Ministan Yaƙi na Burkina Faso, Celestin Simpore, ya ce manufar tattaunawar ita ce fayyace tsare-tsare da ayyukan jami'an haɗin gwiwar.
An gudanar da wannan taro ne a daidai lokacin da hare-haren masu iƙirarin jihadi suka sake ƙazancewa, inda aka kai manyan hare-hare a Mali da Burkina Faso. Waɗannan hare-haren na da alaƙa da ƙungiyar Jama'at Nusrat al-Islam wal-Muslimin (JNIM) mai alaƙa da al-Qaeda.
Simpore ya ce: "Dole rundunar haɗin gwiwar ta tashi tsaye wajen yaƙi da ta'addanci. Dole ne mu shirya domin fuskantar faɗa na gaske."

